Burina a rayuwa shine na zamo shugabar ƙasa mace ta farko a Nigeria ko gwamna a jihar kano – zainab nasir - NAIJA STICK

Mobile Menu

Powered by Blogger.

Top Ads

More News

logoblog

Burina a rayuwa shine na zamo shugabar ƙasa mace ta farko a Nigeria ko gwamna a jihar kano – zainab nasir

Aug 16, 2023


Fitacciyar matashiyar ƴar gwagwarmayar nan wacce ta yi suna wajen jawo cece-ku-ce musamman a sabbin kafafen sadarwa na zamani (Social Media), da ƙoƙarin kare haƙƙin al’umma da ayyukan jinƙai, Zainab Nasir Ahmad ta bayyana cewa ba ta da wani buri a rayuwarta da ya wuce ta ga ta Shugabanci Nageriya ko kuma ta zama gwamnan Jihar Kano domin ta shawo kan matsalolin da su ka gagari maza.


Zainab ta bayyana haka a ya yin tattaunawarta da Dokin Ƙarfe TV, inda ta kuma ƙara da cewa ta na da cikakken fata da ƙwarin gwiwar cewa burinta na zama shugabar ƙasa ko gwamnan Jihar Kano zai cika. “Ba na damuwa da maganganun mutane a kaina, domin ina hango nasara, na kuma tabbata zan kai ga cimma burina”. Cewar Zainab Naseer.


“Ina son mulkar Nageriya ko Jihar Kano domin na kawo ƙarshen matsalolin da su ka dame mu kamar matsalar fyaɗe ga yara da mata da matsalar rashawa da cin hanci da kuma matsalar ta’addanci waɗanda maza sun gaza magance su. Ina da burin ganin na bunƙasa tattalin arziƙi tayadda matasa za su samu ayyukan yi na kawar da talauci a Nageriya ko Jihar Kano jama’a su rayu cikin walwala da cigaban rayuwa ta kowane fanni”. Cewar Zainab Naseer.



Dangane da gurguwar fahimtar da wasu Al’umma su ke da ita kan shugabancin mata kuwa, Zainab ta bayyana cewa “ko a tarihin Musulunci na can asali mata ba ƙashin yasarwa ba ne a fannin ba da gudunmawa ga cigaban al’umma. Misali:


Manzon Allah (S.A.W) ya samu nasarar yaɗa addinin musulunci da gudunmawar mata iyalinsa. Matarsa Nana Khadija gawurtacciyar ƴar kasuwa ce wacce Allah Ya azurta da tarin dukiya. Nana Khadija ta taimakawa manzon Allah (S.A.W) da gudunmawar kuɗin gudanar da da’awa da gudunmawar shawarwari da gudunmawar kykkyawar ɗabi’a tare da ƙarfafa masa gwiwa kan aikinsa na isar da saƙon Allah (Manzanci), wannan wani misali ne da ke nuna jarumta da sadaukarwar mata kan al’umma”. Cewar Zainab.


Zainab ta kuma ƙara da cewa: “Ko da a fannin ilimi da karantarwa ba a bar mata a baya ba domin kuwa mafi yawan shahararrun malaman da su ka tattara hadisan manzon Allah (S.A.W) a farko-farko mata ne su ka karantar da su. Misali: Ibn Hajar ya ɗauki darasi a wurin mata kimanin 53. Shi ma As-Sakhawi ya yi karatu a wurin mata kimanin 68. Imam Suyuti shi ma ya yi karatu a wurin mata kimanin 33”. Inji ta.