Daddy hikima abale yayi magana ta hikima akan halin da Adam a zango yake ciki - Naija Stick

Mobile Menu

Powered by Blogger.

Top Ads

More News

logoblog

Daddy hikima abale yayi magana ta hikima akan halin da Adam a zango yake ciki

Apr 16, 2024


Daddy hikima abale yayi magana ta hikima akan halin da Adam a zango yake ciki


Adam a zango abun na ci masa tuwo a kwarya a duk lokacin da ake jifarsa da kalma auri saki.


A nan shawara biyu ce daddy hikima abale yake baiwa ta farko adam a zango da kuma ita kanta masana’atar Kannywood.


Saboda halin da adamu yake ciki a yanzu ko yau ko gobe kowa zai iya tsintar kansa a wannan yanayin saboda inda kai jarumi ne, darakta ko furodusa dole zaka iya tsintar kanka a wannan halin, to abinda ya kamata a jashi a ciki aji minene matsalar sa ta ina za’a taimake sa, haka shima sai aji shawarwarin da za’a bashi ko minene tsanani akwai sauki a cikinsa.


Da farko Adamu karka manta duk abinda yayi tsanani karka manta Allah , Allah shi yake yi, ba mai bayar da shiriya ko rahama sai Allah ya kamata a nuna masa ga yadda rayuwa take ciki dukkan rayuwar da ka tsinci kanka a ciki da addu’o’i da manzon Allah (s.a.w) ya koya mana ko damuwa kakeji kayi sallati Allah zai sanyaya sauki a zuciyarka.”inji daddy hikima abale.


Ta yaya muke rayuwa a kannywood?

 

Yan kannywood 60% muna rayuwa ba dan Allah ba, idan zanyi rayuwa da wane minene zan samu to kuma wannan ba rayuwa ba ce ta addini ba ya kamata mu gyara wannan matsalolin mu, yau wane ya tafi gobe wane ya tafi gobe kai ne, gobe nine ba wanda ya sani to ko minene rayuwa kada ka manta Allah, allah ya datar damu Allah yasa mudace.