Bola Ahmad Tinubu ya dakatarda ta Beta Edu Ministan Jinkai da again gaggawa - NAIJA STICK

Mobile Menu

Powered by Blogger.

Top Ads

More News

logoblog

Bola Ahmad Tinubu ya dakatarda ta Beta Edu Ministan Jinkai da again gaggawa

Jan 8, 2024


Bola Ahmad Tinubu ya dakatarda ta Beta Edu Ministan Jinkai da again gaggawa


A daidai lokacin da ya sha alwashin tabbatar da gaskiya da gaskiya da rikon amana a cikin tafiyar da mulkin talakawan Najeriya, shugaba Bola Tinubu ya dakatar da ministar harkokin jin kai da yaki da fatara, Dr. Betta Edu daga mukaminsa ba tare da bata lokaci ba. Mai bawa shugaban kasa shawara na musamman akan kafafun midiya Chief Ajuri Ngelale ya fitar da wannan sanarwa.


Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya dakatar da Ministar Ma’aikatar Jinkai Betta Edu kan zargin badakalar miliyoyin kudade.


An dakatar da Minista Edu ne kwana guda bayan shugaban kasar ya umarci a gudanar da bincike a kanta bisa zargin badakalar naira miliyan 585.


Shugaba Tinubu ya bai wa EFCC umarnin gudanar da bincike mai zurfi kan duk wasu hada-hadar kudi na Hukumar Kula da Ayyukan Jinkai ta Nijeriya


Haka kuma shugaban kasar ya bayar ga umarni ga babban sakataren hukumar ya karbi ragamar jagorancin hukumar, tare da bukatar ministar kan ta bai wa hukumomi hadin kai domin gudanar da bincike a kanta.


An yi ce-ce-ku-ce tun daga makon da ya gabata bayan wasu takardu sun nuna cewa Ministar Jinkai Betta Edu ta bayar da umarni ga Akanta Janar ta Nijeriya ta tura naira miliyan 585 ga asusun wata mata mai suna Onlyelu Bridget Mojso a matsayin tallafi na shirin bayar da kudi ga marasa galihu.


Sai dai Akanta Janar ta Nijeriya Dakta Oluwatoyin Madein ta ce ofishinta ba ya biyan kudi a madadin ma’aikatu da hukumomin gwamnati kan ayyukan da suke aiwatarwa.


Bayan da ce-ce-ku-cen ya soma yawa sai Shugaba Tinubu ya bayar da umarni a soma bincike kan wannan lamarin inda daga aka dakatar da ita.